Wasu yanmata 4 sun nutse a kogi sun mutu a kauyen Kafin Doki Yamma dake yankin karamar hukumar Gwaram a nan jihar Jigawa.
Kakakin rundunar yan sandar jihar jigawa SP Abdu Jinjiri ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a Dutse.
A cewarsa lamarin ya faru ne a safiyar jiya talata a lokacin da yaran suke kokarin tsallake kogin domin zuwa gona.
Ya kara da cewa yanmatan hudu da suka mutu sun hada Bilkisu Haruna mai shekara 17, Shamsiyya Nuhu yar shekara 13, da Maryam Danlami shekara 12 da kuma Marakisiyya Musa mai shekara 13 a duniya, dukkanin su yan asalin kauyen Kafin Doki ne dake mazabar Sara a karkashin karamar hukumar Gwaram.
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
- EFCC sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da ke Abuja
- Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP a Najeriya ya bayyana goyon bayansa ga Umar Damagum
- MƊD za ta ƙaddamar da asusun neman taimako domin samar da kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza
- Gwamnan Jihar Jigawa ya nemi ma’aikatun jihar da su cimma yarjejjeniyar da jihar ta kulla da Ofishin FCDO
Abdu Jinjiri ya kara da cewa ansamu nasarar tsamo gawar uku daga cikin su, sannan ana ci gaba da neman daya gawar.
Kazalika ya kara da cewa likita ya tabbatar da mutuwar wadanda akayi nasarar samun gawar ta su.