

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Kakakin majalisar dokokin jihar kano Hamisu Ibrahim ya bayyana damuwarsa dangane da yawaitar mata masu juna biyu da ke rasa rayuwarsu a lokacin haihuwa a duka sassan jihar.
Kakakin ya kuma ce majalisar tana shirin kaddamar da shirin duba lafiyar masu juna biyu da kananan yara kyawta.
Hamisu Ibrahim ya bayyana hakan a wajen zaman kwamatin majalisar mai yaki da illar da kuma manyan masu ruwa da tsaki a majalisar wanda ya gudana a jihar kaduna. Kazalika kakakin yabada tabbacin aiki tukuru domin ganin an nemo bakin zaren matsalar tare da fatan samun kyakkyawan sakamako.