

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya shigar da yara dubu 3, yawancinsu yayan talakawa, a manyan makarantu na musamman guda 2 dake kananan hukumomin Maiduguri da Jere.
Gwamnatinsa ce ta gina makarantun a yankunan kananan hukumomin Maiduguri da Jere dake da yaran dayawa da basa zuwa makaranta. An shirya makarantun da nufin kula da karatunsu.
- An samu tashin gobara a helkwatar sojin Najeriya
- Daliba mace ta farko dake koyon ilmin tukin motar hakar kasa a Sin
- Yadda Najeriya ta karbi allurar Korona
- Najeriya zata karbi rigakafin Corona a gobe Talata
- Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ya ziyarci jamiar Sule Lamido
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mallam Isa Gusau, ya fitar, tace gwamna Zulum ya sanar a ranar Litinin yayin bude makarantun cewa gwamnati zata mika su ga al’umma domin su gudanar da su, yayin da gwamnatin zata biya albashin malamai.
A wani cigaban kuma, gwamnan ya kaddamar da sabon titin da magudanan ruwa a unguwar Maromaro dake Maiduguri.