

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Akalla mutane biyar ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata, bayan da aka yi ruwan sama tare da iska mai karfi wacce ta yi barna a Damaturu, babban birnin jihar Yobe.
An rawaito cewa lamarin ya kuma lalata gidaje sama da 100.
Babban sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, Mohammed Goje, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar jiya.
Ya ce tawagar hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Yobe a jiya, sun amsa kiran gaggawa da wasu mutane nagari suka yi, tare da tallafa musu wajen kwashe wadanda abin ya shafa zuwa asibitin kwararru na jihar Yobe.
Mohammed Goje ya kara da cewa mutanen 41 da lamarin ya shafa, biyar daga cikinsu sun mutu, kuma sun fito ne daga al’ummomi da wurare daban-daban guda 6 a babban birnin jihar sannan an kai su asibiti.