

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Ma’aikatan ceto a kasar Somalia sun ce akalla mutane 6 ne suka mutu kuma wasu dayawa suka jikkata a wani harin kunar bakin wake a Mogadishu babban birnin kasar.
Kungiyar masu da’awar jihadi ta al-Shababa ta dauki alhakin kai harin.
Kakakin kungiyar, Abdiasis Abu Musab, yace dan kunar bakin waken ya nufi wata karamar motar bus cike da masu zabe wadanda ke zaben ‘yan majalisar dokokin kasar.
Dayawa daga cikin wadanda suka mutu masu tafiya a kafa ne a gefen titi.
Ana cigaba da samun yawaitar hare-hare cikin ‘yan makonninnan daidai lokacin da ‘yan siyasa ke kokarin samun damar zaman ‘yan majalisa domin zabar sabuwar gwamnati da shugaban kasa.
Masu sharhi kan harkokin tsaro sun ce ‘yan siyasa na bangaren adawa ne suka kitsa mafiya yawan hare-haren, wasu ta hanyar kungiyar al-Shabab, wadanda mayakansu ke aiwatar da kashe-kashe a madadinsu.