Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo ya amince da cewa miliyoyin ‘yan Najeriya na fama da bakin talauci.
Yace shugabannin da aka zaba a yanzu, zasu zama na jeka na yi ka matukar basu hada kai ba wajen magance abinda da ya kira matsalolin dake neman tarwatsa kasarnan ba.
Osinbajo ya fadi hakan ne yayin bikin rufe taron wuni biyu tsakanin bangaren zartarwa da majalisa wanda aka gudanar a fadar shugaban kasa dake Abuja.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
Yace akwai bukatar yan bangaren zartarwa da yan majalisa su hada kai muddin suna gudun bawa yan Najeriya kunya, wadanda suka basu damar rike mukaman siyasa a manyan matakai.
A takardar bayan taro da aka fitar a karshe taron, wadanda suka halarci taron, sun nemi a samar da shiri mai inganci na sansanta juna tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa, domin cigaban kasa.