An Kama Daya Daga Cikin Mutane Hudu Da Ake Zargi A Kisan Kare Dangi Na Kasar Rwanda A Shekarar 1994

0 73

An kama daya daga cikin mutane hudu da suka tsere wadanda ake zargi a kisan kare dangi na kasar Rwanda a shekarar 1994.

Masu gabatar da kara na Majalisar Dinkin Duniya sun ce an kama Fulgence Kayishema a kasar Afirka ta Kudu kuma ana sa ran zai fuskanci shari’a a Rwanda.

An tuhumi tsohon sufeton ‘yan sandan ne a shekara ta 2001 kan wani lamari da ya faru a lokacin da aka kashe maza da mata da yara ‘yan kabilar Tutsi sama da dubu biyu a cikin wata cocin Katolika da suka nemi mafaka.

An kashe ‘yan kabilar Tutsi da ‘yan kabilar Hutu masu matsakaicin ra’ayi kimanin dubu 800 a kisan kiyashin.

A cewar tuhumar, ana zargin Fulgence Kayishema da tsarawa da aiwatar da kisan gillar wasu mutane dake neman mafaka a cocin a ranar 15 ga Afrilun shekarar 1994.

Daga nan aka binne gawarwakinsu a cikin manyan kaburbura.

Leave a Reply

%d bloggers like this: