An maka kamfanonin sadarwar wayar salula ƙara saboda rufe hanyoyin sadarwar a jihar Zamfara

0 162

Wata kungiyar farar hula mai suna Zamfara Circle, ta maka kamfanonin sadarwar wayar salula kara a gaban kotu tana neman a biya su diyyar naira miliyan 100 saboda rufe hanyoyin sadarwar wayar salula a jihar.

Kamfanonin MTN, Glo, 9mobile da kuma Airtel sune wadanda ake tuhuma a karar.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan jihar da kuma hukumar sadarwa ta kasa (NCC) suna daga cikin wadanda ake tuhuma a karar.

Gwamna Matawalle ya bayar da umarnin dakatar da hanyoyin sadarwar wayar salula a jihar a wani mataki na magance matsalar rashin tsaro.

An dawo da hanyoyin sadarwar a wasu sassan jihar bayan an duba yanayin tsaro amma har yanzu kananan hukumomi shida ba su da hanyoyin sadarwar wayar hannu.

A karar da aka shigar a wata kotu da ke Gusau babban birnin jihar, kungiyar ta Zamfara Circle, ta ce rufe hanyoyin sadarwar ya jawo wahalhalu da asara ga masu amfani da wayoyin hannun.

Leave a Reply

%d bloggers like this: