

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Kwamatin Lura da wurin da za’a gudanar da taron Jam’iyar APC na Kasa tare da Kawata shi, ya ziyarci dandalin Eagle Square da ke birnin tarayya Abuja a cigaba da shirye-shiryen taron Jam’iyar wanda ke tafe.
Shugaban Kwamatin kuma Gwamnan Jihar Plateau Simon Lalong, da ya ke Jawabi bayan duba wurin a ranar Juma’a a Abuja, ya ce ziyarar tana daga cikin shirye-shiryen taron Jam’iyar wanda ke tafe a sati mai zuwa.
Haka kuma ya ce Kwamatin ya na tattaunawa da sauran masu ruwa da tsaki da kuma Kungiyoyi domin tabbatar da cewa an sanya dukkanin abubuwan da ake bukata a wurin Kafin cikar lokacin taron.
Mista Lalong, ya ce Kwamatin sa, ya na aiki tare da Jami’an tsaro domin tabbatar da cewa an gudanar da zaben shugabannin Cikin Nasara ba tare da matsala ba.
Jam’iyar APC zata gudanar da taron ta na kasa a ranar 26 ga watan Maris din da muke ciki.