

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa babu wani cigaba da aka samu wajen kawo karshen yajin aikin gargadi da kungiyar ta shiga.
Yajin aikin kungiyar wanda a yanzu ya shiga mako na 4, an fara shi ne sanadiyyar bukatun kungiyar na gyaran jami’o’in gwamnati na kasarnan da alawus-alawus na malamai tare da yarjejeniyar da kungiyar ta kulla tsakaninta da gwamnatin tarayya da kuma rashin daidaiton manjahar biyan albashi ta IPPIS.
Farfesa Osodeke, wanda ya bayyana a wani shirin gidan talabijin na Channels, ya bayyana takaicinsa kan abubuwan da suke faruwa da kuma gazawar gwamnati wajen cika alkawarukan da ta dauka shekaru biyu da suka gabata.
Shugaban ASUU ya koka bisa abinda ya kira shakulatun bangaro daga gwamnatin tarayya wajen kula da tsarin jami’o’in gwamnati, kasancewar za a iya biya musu bukatunsa a zaman ganawa tsakanin dukkanin bangarorin.