Dalilan da ya sa muka hana tashe a Kano – Ƴan sanda

0 152

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta hana yin tashe a jihar ne saboda yadda wasu ɓata- gari ke amfani da lokacin tashe wajen yin faɗace-faɗacen daba.

A cewar kakakin ‘yan sandan ta Kano, DSP Abdulahi Haruna Kiyawa, hana yin tashe mataki ne na kare al’adar da masu shaye-shaye, da fadan daban ke san lalatawa.

Tashe dai dadaddiyar al’adace da aka shafe shekaru masu yawa ana yi a kasashen Hausa, a cikin watan azumi.

Ga dai karin bayanin da DSP Abdullahi Haruna Kiyawan ya yiwa Khalifa Shehu Dokaji kan matakin da suka dauka:

Leave a Reply

%d bloggers like this: