

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Wasu tsoffin yan Majalisar Jiha dana tarayya a lokacin gwamnatin Sule Lamido, sun fice daga Jam’iyar PDP zuwa Jam’iyar NNPP.
Shugaban Jam’iyar NNPP na rikon Kwarya Musa Bako Aujara, shine ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan gama taron masu ruwa da tsaki a Ofishin Jam’iyar da ke Dutse.
A cewarsa, tsoffin Kwamishinonin, da yan Majalisar Jihar da kuma magoya bayan su, sun fita daga Jam’iyar PDP zuwa NNPP saboda karfa-karfar Jam’iyar PDP da kuma rashin sanin inda ta dosa.
Hon Aujara, ya ce Jam’iyun PDP da APC sun gaza ta kowacce fuska, biyo bayan yadda suka kasa ciyar da kasar nan gaba tare da kyautatawa Talakawa.
Haka kuma ya ce yan Najeriya sun gaji da karerayin APC da PDP, inda ya ce Jam’iyar NNPP ce kadai mafita ga yan Najeriya.
Kazalika, ya ce Jam’iyar NNPP ta yi wani shiri na karbe iko daga hannun Jam’iyar APC a shekarar 2023.