

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Gwamnan Jihar Plateau Simon Lalong, ya ce Delegates din Jam’iyar APC na Jihar zasu zabi Rotimi Amaechi, a matsayin dan takarar shugaban kasa na Jam’iyar a zaben fidda gwani da ke tafe.
Da yake jawabi ga Amaechi da Delegates na Jam’iyar APC a gidan Gwamnati da ke Jos a jiya, Gwamna Lalong, ya ce Rotimi Amaechi ya yiwa mutanen Jihar Alkhairai da yawa.
Gwamna Lalong ya ce ya koyi abubuwa da dama daga wurin Amaechi ta fannin shugabanci nagari.
A jawabinsa, Shugaban masu Rinjaye na Majalisar Dokokin Jihar Plateau, Hon Ibrahim Baba, ya ce Amaechi ya cancani zama shugaban kasa.
Tun farko a jawabin sa, Mista Rotimi Amaechi, ya ce zai samar da ayyukan yi ga Matasa da inganta fannin Lafiya, tare da inganta tsaro matukar ya zama shugaban kasa.