- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Gamayyar kungiyoyin mata 229 sun yi Allah-wadai da Majalisun kasarnan kan kin amincewa da duk wani kudirin doka da ya shafi mata, yayin kada kuri’a kan gyaran kundin tsarin mulkin kasarnan na shekarar 1999 da aka yi jiya.
Kungiyoyin, a cikin wata sanarwa, sun bayyana cewa abin bakin ciki ne matakin da ‘yan majalisar suka dauka na hana mata karin dama da samun wakilci a harkokin Mulki.
A cewarsu majalisun sun yi magana da babbar murya cewa ba sa son cigaban iyayensu mata da ’yan uwansu mata da kuma ‘ya’yansu mata.
Daga cikin kudirori 68, kimanin kudirori biyar ne suka nemi inganta karin damarmaki ga mata a jam’iyyun siyasa, mulki da kuma al’umma baki daya kuma anyi watsi da dukkanninsu.
A wata sanarwa da kungiyoyin matan suka fitar ga manema labarai sun ce ‘yan majalisar sun zabi tauye mata hakkin mata. Kungiyoyin sun kuma shirya gudanar da zanga-zanga a zauren majalisar a yau domin neman biyan bukatunsu.