

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashi ne sun harbe wani jami’in ɗan sandan Najeriya a Jihar Ondo da ke kudancin ƙasar.
Kakakin ‘yan sanda a Ondo, DSP Funmilayo Odunlami, ta shaida wa kafar talabijin ta Channels TV ranar Talata cewa lamarin ya faru ne a Oka-Akoko na Ƙaramar Hukumar Akoko ta Yamma.
Mazauna yankin sun shiga ruɗani sakamakon faruwar lamarin da tsakar ranar Talata bayan maharan sun isa a babura, inda suka harbe ɗan sandan kuma suka ƙara gaba.
Ta ƙara da cewa tuni suka ƙaddamar da bincike don gano waɗanda suka aikata kisan.
An kai gawar jami’in wanda ba a bayyana sunansa ba mutuware na wani asibiti da ke kusa.
Asalin Labarin: BBCHausa