

A wani yunkurin nuna tausayawa da jin kai ga yan kasuwar garin Shuwarin, gwamnan jihar Jigawa Alh. Muhammad Badaru Abubakar ya yarda a dawo cin kasuwar mako-mako bayan da ya bayar da umarnin kulleta cikin makon nan.
Tun farko gwamnan ya sanya an kulle kasuwar ne saboda kin yin biyayya da dokokin matakan kariya daga annobar Korona da aka shinfida ga kowacce kasuwa a jihar.

Sai dai matar na tuba ba ta rasa miji, shugabannin yan kasuwar sun kaiwa gwamnan ziyara tare da alƙawarin bin dokoki matukar ya amince suka dawo hada-hadarsu.
Hakan ta sanya gwamna Badaru amincewa tare da yi musu gargadi a matsayin damar karshe gare su.
- Shugaba Buhari a ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta rayuwar ‘yan Najeriya duk da mummunan yanayi na zamantakewa da tattalin arziki
- ‘Yan bindiga sun kashe jami’in Hukumar Shige da fice ta kasa 1 tare da raunata wasu 2 a karamar hukumar Birniwa
- Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta dakile wani yunkurin yin garkuwa da dagaci
- The National Bureau of Statistics says the aggregate production of mineral products in Nigeria grew from 64.29 million tons in 2020 to 89.48 million tons in 2021
- Shugaban Kasa Buhari ya taya murna ga ministan sadarwa bisa karrama a matsayin zama cikakken dan cibiyar tsaron hanyoyin sadarwa
Babban Mataimaki na Musamman Ga Gwamnan Jihar Jigawa a kan Kafafan sadarwar zamani Auwal D Sankara, ya bayyana cewa gwamna Badaru ya fi bayar da fifiko kan lafiyar jama’arsa fiye da batun ribar kasuwanci.
Shugaban yan Kasuwar Alhaji Muhammad Adamu wanda ya samu jagorancin shugaban majalisar dokokin jihar Alhaji Idris Garba Jahun sun roki gwamnan da ya amince ya bawa yan kasuwar wata damar, sun yarda zasu bi duk ka’idodin da aka shinfida.

Shi ma shugaban karamar hukumar Kiyawa Malam Isyaku Adamu yayi gargadin cewa zasu dauki tsattsauran mataki kan duk wanda aka samu yaki bin dokar, domin shi da kansa zai jagoranci kwamitin da zai na kula da al’amuran kasuwannin.