

Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a jiya yayi bayanin dalilan da suka sanya aka samu rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnonin APC dangane da lokacin gudanar da babban taron kasa na jam’iyyar mai mulki.
Nasir El-Rufai ya sanar da haka bayan gwamnonin na APC sun gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari domin yi masa bayani dangane da matsalolin da ake fuskanta kafin babban taron.
A baya an shirya gudanar da babban taron a ranar Asabar mai zuwa amma kwamitin rikon kwaryar jam’iyyar na kasa a ranar Litinin ya sanar da dage taron zuwa ranar 26 ga watan gobe na Maris.
Biyo bayan ganawa da shugaban kasa a jiya, Nasir El-Rufai ya amince cewa batun babban taron jam’iyyar ya raba kawunan gwamnonin APC.
Amma gwamnan na jihar Kaduna yace ba son zuciya bane ya haifar da rabuwar kawunan ba.