Gwamnatin Jihar Kano ta rufe wasu Asibitoci masu zaman kansu, biyo bayan samun rahoton mutuwar mutane 2

0 77

Gwamnatin Jihar Kano ta rufe wasu Asibitoci masu zaman kansu, biyo bayan samun rahoton mutuwar mutane 2 cikin watanni 6 a Asibitocin.

Hukumar da take Lura da Asibitoci Masu Zaman Kansu ta Jihar ce ta ce ta rufe Asibitin Green-Olives wanda ke kan Sabon Titin Tal’udu a Gadon Kaya, ta Karamar hukumar Gwale, biyo bayan samun rahoton mutuwar mutane 2 a Asibitin.

Sakataren Zartarwar na Hukumar Dr Usman Tijjani Aliyu, shine ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, inda ya ce hukumar ta binciki lamarin kuma ta gano gaskiya kan zarge-zargen da ake yiwa Asibitin na rashin bawa marasa lafiya kulawar data kamata.

Dr Usman Tijjani ya bukaci Al’umma su kai rahoton Asibitocin da ake samun labarin cin zarafin marasa lafiya ko kuma nuna rashin kwarewar aiki.

Leave a Reply

%d bloggers like this: