

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin jihar Neja ta yi kira ga hukumar kula da shige da fice ta kasa immigration da ta taimaka wajen duba kwararar bakin haure cikin jihar a wani mataki na kokarin magance rashin tsaro.
Sakataren gwamnatin jihar Ahmed Ibrahim Matane ne ya yi wannan roko a lokacin da sabon kwanturolan immigration na jihar Nongo Samuel Shima ya kai masa ziyara.
A wani lamari makamancin wannan, ‘yan bindiga sun kai farmaki a kauyukan gundumar Bashar da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato.
Wani mazaunin daya daga cikin kauyukan ya shaidawa manema labarai cewa dagatan kauyukan da wasu mazauna kauyukan sun tsere.
Wani mazaunin kauyukan shima ya shaida wa manema labarai cewa suma suna shirin tserewa saboda masu garkuwa da mutane sun mamaye kauyukan kuma suna kai musu farmaki a kowace rana.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Ubah Gabriel, bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba akan lamarin.