Gwamnatin kasar Nijar ta hana fitar da dabbobin zuwa ƙasashen waje

0 183

Masu shirin gudanar da ibadar layya musamman a Najeriya sun fara bayyana fargabarsu kan tashin farashin dabbobin layya, sakamakon matakin da gwamnatin Nijar ta ɗauka na hana fitar da dabbobin zuwa ƙasashen waje.

A makon da ya gabata ne gwamnatin ƙasar ta Nijar ta bayyana matakin haramta fitar da dabbobi zuwa ƙasashen waje.

Cikin sanarwar haramcin da ministan ƙasar, Abdoulaye Seydou ya bayyana, ya ce gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakin ne domin tabbatar da samar da wadatuwarsu a kasuwannin ƙasar a wani mataki na karya farashin dabbobin gabanin bukukuwan Sallar Layya.

Jamhuriyar Nijar na daga cikin ƙasashen da ke kan gaba wajen samar da dabbobin layya, a yankin yammacin Afirka.

Leave a Reply