

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa a shirye take ta kwashe ƴan ƙasarta da ke son barin Ukraine bayan Rasha ta kutsa ƙasar.
A wata sanarwa da gwamnatin Najeriyar ta fitar ta hannun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, ta ce ta yi mamaki kan harin da Rasha ta kai ƙasar.
Wata mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Francisca Omayuli ta bayyana cewa ofishin jakadancin Najeriya a Ukraine ya tabbatar mata da cewa ƴan Najeriya da ke Ukraine za su kasance cikin tsaro kuma ana ɗaukar matakai na kwashe waɗanda suke so su bar ƙasar