

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shirya-shiryen inganta albashin malaman makaranta da kuma yayayin ayyukansu.
Karamin ministan ilimi Chukwuemeka Uwajiuba, ya bayyana haka jiya Alhamis a birnin Benin yayin bikin yaye wanda suka kammala samun horon koyarwa da aka gudanar.
Yayin da babban mai bashi shawara Misis Muna Onuzo-Adetona ta wakilce shi a taron, yace gwamnati mai ci zata cigaba da yin duk mai yuwa wajen bunkasa harkokin ilimin kasar nan tare da warware duk wasu matsaloli da ka iya kawo tazgaro a tsarin koyarwa.
Yayi bayanin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari yana cigaba da aiki tukuru domin ganin yadda za’a inganta da sake fasalin tsarin koyarwa da zai yi dai-dai da zamani, musamman wajen samar da kwarrun Malamai domin gogayya da sauran kasashen da suka ci gaba a duniya.
A cewarsa gwamnatin tarayya ta bayyana malaman makarantu matsayin tubalin gini kasa, da haka ya amince kara musu wa’adin aiki daga kan shekara 60-65 da haihuwa, da kuma kara wa’adin aikin daga shakara 35-40.