

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin tarayya ta yi alkawarin kammala kasuwar zinare da ta fara ginawa a Kano nan da watanni 10.
Ministan tama da karafa, Olamilekan Adegbite, ya sanar da haka yayin rangadi a kasuwar da ake ginawa a Kano, kamar yadda yazo cikin sanarwar da kakakin ma’aikatarsa ya fitar.
A wani labarin kuma, kotun daukaka kara a Kano ta dage sauraron karar da ake yiwa Yahaya Sharif Aminu dan shekara 22 wanda a bara aka janye hukuncin kisan da aka yanke masa bisa zarginsa da yin batanci ga fiyayyen halitta.
Dage sauraron karar ya biyo bayan bukatar gwamnatin jihar Kano a jiya ta neman karin lokaci domin fitar da martani dangane da daukaka karar da Yahaya Aminu yayi.
Tuni gwamnatin jihar ta yi jinkirin watanni 11 kafin fitar da martaninta, kasancewar an mika mita kama bayanin wanda ake kara a watan Maris na bara.