

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin Tarayya tana shirin samar da ayyukan yi miliyan 21 ta hanyar samar da gine-ginen gwamnati sosai da ayyuka nan da shekaru uku masu zuwa.
Karamin ministan kudi, kasafin kudi da tsare-tsaren kasa, Clem Agba, shine ya fadi haka jiya a Abuja a wajen taron karawa juna sani na kwanaki 5.
Hukumar cigaban tarayyar Afirka da wata kungiyar cigaban Afirka ne suka hada taron.
Yace matakin samar da ayyukan yi miliyan 21 na daya daga cikin makomar shirin cigaban kasarnan wanda yake neman fitar da mutane miliyan 35 daga kangin talauci nan da shekarar 2025.
Yace wannan zai kafa danbar cika alkawarin gwamnati mai ci na fitar da mutane miliyan 100 daga kangin talauci daga nan zuwa shekarar 2032.