Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roki masu kwatanta ayyukansa da na sauran gwamnoni su daina.
Ya yi rokon ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Isa Gasau ya fitar jiya Litinin.
Gwamnan ya yabawa mutanen da ke tallata ayyukansa a shafukan sada zumunta, sai dai ya ce bai kamata a rika kwatanta ayyukansa da na sauran gwamnoni ba, tun da dukkan jihohin suna da bambanci.
Amma yana matukar godiya bisa dukkan goyon baya da tallata ayyukansa da mutane sukeyi a kwanakin nan.
Ya kuma ce yana samun sakonni, inda ake kwatanta ayyukan da da yakeyi yi a Borno da cewa sun zarta na wasu jihohi.
Ya kara da cewa Gaskiya bayajin dadi a duk lokacin da aka kwatanta shi da wani gwamna ta hanyar muzanta shi, musamman idan wadanda suke yin hakan suna cikin masu amfani da shafukan sada zumunta.