

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Hukumar Asusun Adashen Gata na Ma’aikatan Jiha da n Kananan Hukumomi ta ce ta raba Naira Biliyan 4 ga Ma’aikata Dubu 12 da 868 da suka yi Riyata cikin shekara 6.
Sakataren Zartarwa na Hukumar Alhaji Kamilu Aliyu Babura, shine ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi karkashin Jagorancin Mista Ambali Akeem wanda suka kawo masa ziyara a Ofishin sa.
A cewarsa, kudaden sun kunshi biyan hakkokin Ma’aikatan da suka yi ritaya da wanda suka mutu da kuma kudaden Fansho na Alawus-Alawus daga shekarar 2015 zuwa 2022.
Kazalika, ya ce kudaden sun hada da Ma’aikatan Jiha da na Kananan Hukumomi da kuma na Sashen Ilimi na Karamar Hukuma.