

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Hukumar bunkasa ilmin addinin musulunci ta jihar Jigawa ta kaddamar da musabakar karatun Al-Qur’ani karo na 36 a Dutse.
A jawabinsa wajen bude musabakar, sakataren gwamnatin jiha, Adamu Abdulkadir Fanini ya jinjinawa gwamnati bisa daukar nauyin musabakar inda ya yi kira ga ‘yan takara da su mayar da hankali.
A jawabinsa, mai bai wa gwamna shawara kan harkokin addini, Mujitafa Sale Kwalam, ya bukaci ‘yan takara da su dauki kansu a matsayin zakaru kasancewar suna halartar musabaka a matakai daban-daban.
Ya kuma yabawa gwamnatin jiha bisa yadda take yiwa addinin musulunci hidima tare da fatan alkalan musabakar zasu kasance masu gaskiya da adalci.
A nasa jawabin shugaban hukumar gudanarwa na hukumar, Khadi Isah Gantsa, ya godewa sakataren zartarwa na hukumar bisa namijin kokarinsa wajen samun nasarar musabaka a matakai daban daban.