

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Hukumar kare fararen hula da civil defence ta yi gargadi kan amfani da wuta a lokutan bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse, mai dauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar a jihar Jigawa, Adamu Shehu.
Adamu Shehu ya shawarci al’ummar jiharnan da su kara taka tsantsan da kuma kula da harkokin tsaro a yayin bukukuwan.
Ya bayyana cewa, a shirye-shiryen da ake yi na gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara a Jihar Jigawa, Kwamandan hukumar a Jihar, Mustapha Talba, ya kuma bayar da umarnin tura jami’ai 750 cikin gaggawa domin ganin an gudanar da bukukuwan lami lafiya a fadin kananan hukumomin jiharnan 27.
Ya kuma yi kira ga al’ummar jiharnan da su kara taka tsan-tsan, su zama masu bin doka da oda, tare da kai rahoton duk wani abu bakon abu da basu yarda da shi ba, zuwa ga hukumar tsaro mafi kusa.