Hukumar INEC ta gano sama da mutane milyan daya da sukayi rijistar katin zabe ba bisa cancanta ba

0 79

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta gano wasu mutane da suka yi rijista sau biyu zuwa sama da wadanda rijistarsu ba ta cancanta ba, a cikin kundin rajistar masu kada kuri’a da aka ci gaba da yi tsakanin ranar 1 ga watan Janairu zuwa 31 ga watan Yuli.

Kwamishinan hukumar INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.

Ya bayyana cewa an gano kura-kuran a lokacin tsaftace rajistar masu kada kuri’a ta hanyar amfani da na’urar tantancewa ta ABIS.

A baya dai hukumar ta bayyana cewa daga cikin rajistar mutane miliyan 2 da dubu 523 da 458 da aka yi tsakanin ranar 28 ga watan Yunin 2021 zuwa ranar 14 ga watan Junairun 2022, an gano sunayen masu rajista miliyan 1 da dubu 126 da 359 ba su da inganci kuma aka yi watsi da su.

Leave a Reply

%d bloggers like this: