Hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta NCDC ta tabbatar samun ƙarin mutum 418 da suka kamu da korona ranar Lahadi a ƙasar.

Cikin rahoton da ta wallafa, NCDC ta ce mutanen sun fito ne daga jiha 12. Jihohin su ne:

  • Lagos-314
  • Ogun-27
  • Plateau-18
  • Edo-17
  • Enugu-11
  • Abia-8
  • Delta-7
  • Bayelsa-5
  • Kano-4
  • Rivers-4
  • Osun-2
  • Oyo-1

Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 217,481 ne suka harbu da cutar tun bayan ɓullarta. Haka nan ta kashe 2,981, sai kuma mutum 207,746 da aka sallama bayan sun warke.

Related Posts

Leave a Reply

%d bloggers like this: