

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa NCDC ta ce an samu rahotan bullar zazzabin Lassa guda 48 cikin wannan shekarar ta 2022.
Rahotan da Cibiyar ta fitar ya yi nuni da cewa an samu rahotan bullar cutar ne daga ranar 3 zuwa 9 ga watan Janeru da muke ciki.
Hukumar ta NCDC ta ce an samu rahotan ne a Kananan Hukumomi 22 na Jihohi 10 da suke kasar nan, ciki harda Bauchi da Edo da kuma Ondo.
Sauran Jihohin sune Taraba, Benue, Kaduna da Plateau da Kogi da Cross River da kuma Ebonyi.
Kwanaki kalilan da suka gabata, hukumar NCDC ta yi gargadin cewa akwai yuwuwar samun barkewar cutar a kasar nan.
An bada rahotan cewa a shekarar 2021, kimanin mutane 102 ne suka mutu a sanadiyar zazzabin Lassar.