

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Hukumar zaɓen ta Kasar Libya ta yi kira da ɗage zaɓen shugaban ƙasa da ya kamata a gudanar a ranar Juma’a mai zuwa.
Hukumar na son a ɗage zaɓen na tsawon wata ɗaya, kuma ta ba da shawarar gudanar da zaɓen a ranar 24 ga watan Janairu bayan tuntuɓar majalisa.
Zaɓen Libya na tattare da ƙalubale musamman cancantar wasu ƴan takarta da kuma barazanar tsaro.
Tun mutuwar Kanal Ghaddafi a 2011 Libya ke fama da rikici. Daga cikin waɗanda aka hana takara har da ɗan tsohon shugaban Saif al-Islam.
Jakadan Kasar Amurka a Libya Rochard Norland, ya bayyana damuwa a madadin Amurka bisa dage lokacin zaben.