

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Rundunar ‘yan sanda a Kano ta kama wani malamin makaranta mai zaman kanta, mai suna Abdulmalik Tanko, wanda ake zargi da yin garkuwa tare da kashe dalibarsa mai suna Hanifa Abubakar ‘yar shekaru biyar.
Ana zargin Abdulmalik Tanko da hada baki da wani mai suna Hashim Isyaku, wanda shi ma yake tsare a hannun ‘yansanda.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar jiya, ya ce wadanda ake zargin sun bukaci iyayen yarinyar da su biya kudin fansa naira miliyan 6.
Hanifa dalibar Abdulmalik Tanko ce a wata makaranta mai zaman kanta da ke Kwanar Dakata a karamar hukumar Nassarawa ta jihar Kano.
A cewar ‘yan sandan, wanda ake zargin ya amsa laifin sa na bawa yarinyar guba a lokacin da ya fahimci cewa ta gane shi.
Daga nan Abdullahi Tanko da Hashim Isyaku suka binne gawarta a wani karamin kabari da suka haka a harabar makarantar da ke Kwanar ’Yan Gana, a Unguwar Tudun Murtala dake karamar hukumar Nassarawa a Jihar Kano.