Kimanin mutane 14 ne suka tsere daga hannun wasu yan Bindiga a jihar Sakkwato

0 103

Kimanin mutane 14 ne suka tsere daga hannun wasu yan Bindiga, wanda suke aiki da Bello Turji, bayan sun shafe tsawon kwanaki suna tsare a hannun su a Jihar Sokoto.

Wasu Majiyoyin sun bayyana cewa mutanen sun tsere ne daga Maboyar Suruddubu, wanda take Karamar Hukumar Isa ta Jihar a ranar Asabar, a lokacin da yan bindigar suka fita aiki.

Shugaban Karamar Hukumar Alhaji Abubakar Yusif, shine ya tabbatar da hakan ga manema labarai ta cikin wayar tarho.

A cewarsa, ya umarci Ma’aikatan Lafiya su bawa mutanen kulawar da ta kamata, biyo bayan raunikan da suka ji a hannun yan bindigar.

Shugaban Karamar Hukumar ta Isa, ya ce 8 daga cikin wadanda suka gudun yan karamar hukumar Sabon Birni ne, 3 kuma yan karamar hukumar Isa ne na Jihar Sokoto.

Haka kuma ya ce sauran mutum 3 yan karamar hukumar Kauran Namoda ne ta Jihar Zamfara.

Kakakin rundunar yan sandan Jihar Sokoto Sanusi Abubakar, bai amsa kiran da manema labarai suka tura masa ba kan batun.

Leave a Reply

%d bloggers like this: