

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Wata Kotun gwamnatin tarayya wanda take zamanta a birnin tarayya Abuja, ta hana hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC dakatar da Rijistar zabe daga ranar 30 ga watan Yunin 2022.
Hukumar INEC ta sanya ranar 30 ga watan Yunin da muke ciki a matsayin ranar dakatar da Rijistar katin zabe, a kasa baki daya a wani yunkuri na cigaba da shirye-shiryen babban zaben shekarar 2023 mai zuwa.
Hukumar Yaki da Cin hanci da rashawa da kuma tabbatar da shugabanci Nagari wato SERAP da kuma wasu yan Najeriya su 185 ne suka shigar da karar hukumar INEC a gaban Kotun.
SERAP ta ce akwai bukatar hukumar INEC ta kara wa’adin cigaba da yin rijistar katin masu zaben, kamar yadda ta yiwa Jam’iyun siyasa a lokacin da suke kokarin yin zaben fidda gwani.
Haka kuma SERAP ta bukaci Kotun ta yiwa dokar kara wa’adin rufe Rijistar zaben fassara, kan ko hakan ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa na 1999 wanda aka sake yiwa kwaskwarima, da kuma Dokar Zabe.