

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Kungiyar lauyoyi masu kare marasa galihu a Najeriya ta ce Abduljabbar Nasiru Kabara bai cancanci samun kariyarsu ba, irin wadda suke bai wa masu karancin gata bayan ficewar lauyansa Ambali Muhammad daga shari’ar da ake yi masa ta yin batanci ga addini.
Wata kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a kofar kudu ce ta nemi a bai wa Abduljabbar kariya daga kungiyar lauyoyin.
Tun daga watan Yunin bara ne yake fuskantar shari’ar yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) wanda gwanati Kano ta ce aikin nasa zai iya tunzura jama’a.
A jiya ne daraktan kungiyar Barista Mukhtar Labaran Usman ya shaida wa wata kotu cewa malamin bai cancanci a ba shi kariya ba saboda yana samun abin da ya wuce naira 30,000 wato mafi karancin albashida kasa ta yarda da shi.