Kungiyyar likitoci masu neman kwarewa ta kasa ta dawo daga yajin aiki

0 61

Kungiyyar likitoci masu neman kwarewa ta kasa ta dawo daga yajin aikin data shafe watanni 2 tana gudanarwa.

Kafin hakan dai tin a ranar 2 ga watan Agusta ne kungiyyar ta shiga yajin aikin, akan abin da ta kira rashin biyan yayan kungiyyarta albashi akan kari da sauran bukatunta.

Wanda masu ruwa da tsaki ciki harda shugaban kasa da kusoson majalissar wakilai suka kasa shawo kan yayan kungiyyyar.

Wannan na zuwa ne bayan kotin ladaftar da ma’aikata ta kasa ta bukaci yayan kungiyyar su dawo daga yajin aikin da suke gudanarwa amma sukayi kunnan uwar shegu da ita.

Yayin da yake tattaunawa da kamfanin dillacin labarai na kasa NAN shugaban kungiyyar Godiya Ishaka yace kungiyyar ta janye daga yajin aikin.

Sun kuma yanke hukuncin ne bayan zaman tattaunawar gaggawa da shuwagabannin kungiyyar suka gudanar, inda suka amince dawowa fara aiki a ranar Laraba mai zuwa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: