Kungoyoyin Masu Dauke Da Makamai Sun Mamaye Asibitoci A Kasar Sudan

0 158

Kungiyar tallafi mai fafutukar kare yara ta yi gargadin cewa kungoyoyin masu dauke da makamai sun mamaye asibitoci a kasar Sudan suna kwashe kayayyakin ceto rayuka.
Kungiyar tallafin tace tun a farkon wannan satin ne mayakan suka fatattaki wasu mutane 8 dake amfani da oxygen a wani asibiti dake Khartoum, babban birnin kasar.
Kungiyar tace an wawashe kayayyakin wasu kananan asibitoci guda 3 na ‘yan gudun hijira a yankin Darfur.
Majalisar dinkin duniya ta neman kimanin euro miliyan dubu 3 cikin gagggawa domin samun kudaden ayyukan jinkai a Sudan.
Majalisar ta dinkin duniya na hasashen cewa sama da mutane miliyan daya ne za su fice daga kasar kasancewar fada na cigaba da muni tsakanin sojoji da mayakan kungiyar RSF.

Leave a Reply