A karon farko tun watan Afrilu, yawan wadanda suka kamu da corona a Najeriya cikin rana guda yayi kasa da 100.
Hukumar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta tabbatar da samun sabbin mutane 79 a jiyar Lahadi da dare, adadi mafi karanci a cikin kusan watanni biyar.
An samu sabbin mutanen a jihoshi 12 da babban birnin tarayya.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
An kuma samu rahoton sabbin mutane 4 da cutar ta hallaka a jiyan, inda jumillar wadanda cutar ta kashe ya kai dubu 1 da 82.
Kazalika, da mutane 64 da suka warke kuma aka sallamesu a jiya, an samu rahoton karancin wadanda suka warke daga cutar a rana guda tun ranar 21 ga watan Mayu.
Daga cikin mutane dubu 56 da 256 da yanzu aka tabbatar sun kamu da cutar corona a jihoshi 36 da babban birnin tarayya, mutane dubu 44 da 152 sun warke.