Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Majalisar Dinkin Duniya ta ce yanzu haka ‘yan gudun hijira miliyan daya ne suka tsere daga Ukraine zuwa kasashe makwabta.
Tserewar dumbin ‘yan gudun hijirar na zuwa ne cikin kwanaki bakwai kacal bayan mamayar kasar da Rasha da ta fara a makon jiya Alhamis.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ta shafin Twitter, kwamishinan hukumar ‘yan gudun hijira na Majalisar Dinkin Duniya, Filippo Grandi, ya roki a tsagaita wuta domin a samar da agajin jin kai na ceton rai ga miliyoyin mutanen da suka rage a kasar.
Hukumar ta yi hasashen rikicin zai raba mutane kimanin miliyan 12 da mahallansu cikin bukatar agaji.