Majalisar Karamar Hukumar Hadejia ta kaddamar da wani kwamiti kan cigaban tsarin tsaftar muhalli

0 53

Majalisar Karamar Hukumar Hadejia ta kaddamar da wani kwamiti mai wakilai 17 kan cigaban tsarin tsaftar muhalli.

Da yake kaddamar da kwamitin, shugaban majalisar, Alhaji Abdulkadir Bala T. O ya ce ana sa ran kwamitin zai yi aiki bisa kiyayewa da sharuddan da aka gindaya masa.

Jami’in yada labarai na karamar hukumar Muhammad Garba Talaki ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya aikawa kafafen yada labarai ciki har da Sawaba.

Sanarwar ta ce an umurci kwamitin da ya gabatar da rahotonsa cikin makonni biyu.

Mambobin kwamitin sun hada da Alhaji Adamu Abdullahi a matsayin Shugaba da Muhammad Abdullahi a matsayin sakatare, yayin da hakimai uku, Babban Limami da jami’in yada labarai da sauransu, suka zama mambobin kwamitin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: