Majalisar wakilai ta kasa za ta gudanar da zama yau domin gyaran dokar zabe ta 2022

0 114

Majalisar wakilai ta kasa za ta gudanar da zama a gobe domin gyaran dokar zabe ta 2022.

Magatakardar majalisar, Yahaya Danzaria, cikin wata sanarwa da ya fitar a yau yace ‘yan majalisar za su zauna domin gyaran wani babban kuskure a dokar.

Tunda farko, majalisar dattawa ta gyara sashe na 84, karamin sashe na 8 na dokar zaben, domin bayar da dama ga manyan deliget suyi zaben cikin gida.

Kudirin, wanda mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ovie Omo-Agege ya gabatar, an zartar da shi yayin zaman majalisar.

A dokar zaben da ake da ita a yanzu, ba a bayar da dama ba ga manyan deliget.

Ovie Omo-Agege ya ambaci manyan deliget da suka hada da shugaban kasa da mataimakinsa da ‘yan majalisun tarayya da gwamnonin jihoshi da mataimakansu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: