

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC.
Da ake sanar da sakamakon zaben wanda aka gudanar a filin taro na Mallam Aminu Kano dake birnin Dutse, an ayyana Umar Namadi a matsayin wanda ya samu nasara da kuri’u dubu 1 da 220, sai Muhammad Sabo Nakudu yazo na biyu da kuri’u 106.
Sanata Ibrahim Hassan Hadejia yazo na uku da kuri’u 58, sai Faruku Adamu Aliyu wanda ya samu kuri’u 15, sai kuma Sani Hussaini Garin Gabas mai kuri’u 5.
Umar Namadi babban akawu kuma ya kafa kamfaninsa na manyan akawu a Kano a shekarar 1993.
A matsayin wanda ya fara rike shugaban sashen asusun kudaden kamfanin Dangote, Umar Namadi shine ya assasa ginshikin samar da bayanan kudaden kamfanin na Dangote a kowane wata.
Tsohon kwamishinan kudi na jihar Jigawa ya kuma kasance wakili a kwamitin tantancewa da tabbatar da kwangiloli da tantance ma’aikata.