Me ya sa jarabawar JAMB ta bana ta bar baya da ƙura?

0 326

Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya, JAMB ta ce daga ranar 16 ga watan Mayun bana ne, za ta bai wa wasu daga cikin ɗaliban da suka fuskanci matsala wajen rubuta jarabawar a bana damar sake rubuta ta.

Ta ce za ta yi hakan ne bayan binciken da ta gudanar wanda ya nuna cewa an samu tangarɗa yayin jarabawar lamarin da ya sa wasu ɗalibai da dama suka faɗi jarabawar.

A sanarwar da JAMB ta fitar ranar Laraba, hukumar ta tabbatar cewa akwai wasu matsaloli da tabbas suka ba da gudummawa wajen faɗuwar da ɗalibai suka yi a jarabawar ta bana.

Shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede dai ya nemi afuwar ɗaliban da suka samu matsala har ma da ƴan Najeriya inda ya ce ya ɗauki alhakin matsalolin da aka samu yana mai alƙawarta cewa za su yi duk mai yiwuwa wajen gyara kuren da aka samu.

Leave a Reply