

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Manajan Darakta na kamfanin man fetur ta kasa NNPC, Mele Kyari, ya bayar da tabbacin kawo karshen dogayen layukan man da ake yi a gidajen mai a kasar.
Mele Kyari ya bayyana haka ne jiya a Abuja lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin wucin gadi na majalisar wakilai kan halin da matatun man kasarnan ke ciki.
Ya ce akwai isasshen man fetur a kasarnan da zai biya bukatun ‘yan kasarnan.
Mele Kyari ya ce NNPC na da jimillar lita miliyan dubu 2 da miliyan 800 na man fetur a kasar nan wanda ya isa ya biya bukatun al’ummar kasar nan na kwanaki 47 masu zuwa ba tare da an shigo da wani daga waje ba.
Ya danganta matsalar karancin man fetur da ake fama da shi a kasar nan da hutun ranar ma’aikata da kuma hutun Sallah.
Manajan Daraktan ya ce tsaikon ya haifar da firgici da ya jawo gaggauta sayen man yana mai cewa hakan ne ya janyo dogayen layukan a gidajen mai.