

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya amince da nadin Usman Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban ma’aikatan jihar.
Har ya zuwa lokacin da aka nada shi, Usman Bala Muhammad, shi ne babban sakatare a ma’aikatar yada labarai ta jihar.
Haka kuma an nada sabbin manyan sakatarori da suka hada da Muhammad Bello Shehu da Magaji Lawan da Bilyaminu Gambo Zubairu da Mairo Audi Dambatta.
A wani labarin kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta dakatar da gudanar da tashe, wanda aka saba farawa daga ranar 10 ga watan Ramadan mai alfarma.
Rundunar ‘yansanda ta ce an dakatar da al’adar ta bana saboda dalilai na tsaro.