Ofishin jekadancin Najeriya ya karɓi ƴan Najeriya 200 daga kasar Ukraine

0 159

Jakadiyar Najeriya a Romania da ke makwabtaka da Ukraine ta ce zuwa yanzu sun karɓi ƴan ƙasar kusan 200 yawancinsu ɗalibai da suka tsallako Bucharest babban birnin ƙasar daga Ukraine.

Safiya Nuhu ta shaida wa BBC cewa suna kyautata zaton samun adadin ƴan Najeriyar fiye da haka da ke tserewa daga Ukraine.

“Mun tarbe su kuma mun ba su masauki a otel otel a Bucharest,” in ji ta.

Ɗaruruwan ƴan Najeriya ne suka tsallaka kan iyakar Ukraine, inda ake sa ran kwashe su zuwa birane mafiya aminci, kafin mayar da su Najeriya.

Sai dai yawancinsu da sauran ƴan Afirka sun yi ƙorafi kan yadda ake nuna masu wariya a kan iyakar Ukraine da Poland.

BBCHausa

Leave a Reply

%d bloggers like this: