Rarara Ya Bukaci Kotu Da Tayi Watsi Da Karar Sa Da Aka Shigar Gabanta

0 73

Fitaccen mawakin siyasar jihar Kano, Dauda Kahutu Rarara, ya bukaci wata babbar kotun shari’ar Musulunci ta jihar da ta yi watsi da karar da aka shigar a gabanta.
Ana tuhumar Dauda Rarara da rashin biyan kudi sama da naira miliyan 10 ga wani dan kasuwa, Muhammad Ma’aji.
A zaman da kotun dake zama a Rijiyar Zaki karkashin jagorancin mai shari’a Halhalatul Khuza’i Zakariyya, lauyan Dauda Rarara ya shaida wa kotun cewa shari’ar ba ta da tushe don haka a yi watsi da ita.
Ya kara da cewa sun bayar da amsarsu a rubuce ga mai kara da kotu, amma masu gabatar da kara sun yi ikirarin cewa sun samu a makare a lokacin da kotu za ta zauna.
Wanda ya shigar da karar, Muhammad Ma’aji, ya shaida wa kotun cewa yana da dukkan shaida a rubuce domin tabbatar da ikirarin nasa tun farkon dangantakarsa kasuwancinsa da Dauda Rarara a shekarar 2021 amma bai biya shi ko sisi ba.
Alkalin kotun ya dage sauraron karar zuwa ranar 12 ga watan Mayu domin ci gaba da sauraro.

Leave a Reply

%d bloggers like this: