Rikici ya barke jiya a unguwar Sabon Gari cikin birnin Kano a jihar Kano

0 84

Rikici ya barke jiya a unguwar Sabon Gari cikin birnin Kano a jihar Kano, bayan wasu matasa sun fara kone-kone.

Unguwar ta Sabon Gari wacce yawanci baki ne ke zama a cikinta, ita ce cibiyar rikicin addini da na kabilanci a jihar.

Majiyoyin tsaro sun gayawa manema labarai cewa rikicin ya fara ne lokacin da jami’an Hisbah suka je domin kama wasu a wajen da ake badala kan titin Ballata.

Shaidu sun ce an samu turmutsitsi a kusa da unguwar ta Sabon Gari bayan bata garin sun cinna wa tayoyi wuta.

Sauran majiyoyin sun ce an kashe wasu mutane tare da raunata wasu da dama a rikicin.

An kasa samun jin ta bakin kakakin rundunar yansandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, dangane da batun.

Leave a Reply

%d bloggers like this: