

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta gargadi masu ababen hawa kan yadda suke lodi fiye da kima da kuma matsalar tukin yara.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun kakakin rundunar, ASP Lawan Shiisu Adam.
Ya ce an yi gargadin ne domin rage yawan hadurran da ke faruwa a fadin jiharnan.
Shiisu Adam ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Sale Tafida, ya umurci dukkan jami’an ‘yan sanda na shiyyar da su fara sintiri sosai.
Sai dai ya umarce su da su kamo tare da gurfanar da direbobi masu lodin da ya wuce kima da masu karancin shekaru a fadin kananan hukumomi 27 na jiharnan, ba tare da bata lokaci ba.
Aliyu Tafida ya kuma jaddada kudirin ‘yan sanda na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasarnan.